Sakamakon Makwaftaka dake tsakaninsu da Jihar Jigawa, musamman Kasar Hadejia, bazakayi minti goma kana zaune ba sai kaci karo da wadannan bayin Allah suna cewa A taimaka mana da sadaka, mu 'yan gudun hijira ne..
A jihar Jigawa dai wadannan 'yan gudun hijira gwamnatin baya bata taba tallafa musu da komai ba, ko gida ko abinci ko sutura, sakamakon Kabilanci da yayi Tasiri a zuciyar tsohon gwamnan, wanda bincike ya nuna cewa abinda yasa ya nuna halin ko in kula ga wadannan mutane shine.. Suna zaune ne a wani bangaren Jihar ta Jigawa wanda kuma shi a zuciyarsa abin bai shafeshi ba.
Abin jira a gani dai shine... Ko sabuwar Gwamnatin Jigawa zata waiwaici wadannan bayin Allah? Ganin cewa wasu da yawa babu abinda zasu koma suyi a garuruwansu, sakamakon Kone musu gidaje da dukiyoyi da kashe musu 'yan-uwa da akayi. Allah ya baiwa sabuwar gwamnati ikon taimakawa......
No comments:
Post a Comment
KA RUBUTA RA'AYINKA!