Tuesday, December 28, 2021

KUNGIYAR HADEJIA INA MAFITA TA KARBI BAKUNCIN KUNGIYAR JIGAWA NORTON WEST..


Daga Nasiru Kainuwa Hadejia. 

Ziyarar wakilai da ga gamayyar ƙungiyoyin masarautar Ringim, zuwa ga ƙungiyar Hadejia Ina Mafita Initiative a yammacin wannan rana. Wanda suka sami tarba da ga wajen shugaban Hadejia Ina Mafita Initiative Sir Baidi Gajo Elleman da mataimakinsa Dr Hussaini Shehu, sakataren ƙungiya Malam Salisu Muhamad Birniwa da sauran MEMBERS na ƙungiya.

Gamayyar ƙungiyoyin ta na wakiltar ƙungiyoyi sama da arba'in (40) na masarautar Ringim, ziyara ce ta sada zumunci tare da yabawa da irin aikace-aikacen da ina Mafita take aiwatarwa.

Gamayyar ƙungiyoyin sun yi jinjina haɗe da godiya ta musamma bisa yadda Ina Mafita ta zama silar samuwar wasu abubuwan alkhairi a  masarautarsu.

Shugaban Kungiyar Hadejia Ina Mafita Initiative Sir Baidi Gajo Elleman. 

Wannan ziyara dai ba abin da take nunawa illa ƙaruwar samuwar danƙon zumunci a tsakanin masarautar Ringim da ta Hadejia wanda dama can haka abin yake mu na da kyakkyawar alaƙa a tsakaninmu. Wannan abin yabawa ne ace yau ƙungiyoyi su na tarayya a  wajen ciyar da jiharsu gaba bisa manufa guda.

Fatanmu a kullum Allah Ya ƙara haɗa kan al'ummar wannan jiha mai albarka, matsalolin da suka kewaye mu mu na roƙon Allah da ya kawo mana mafita.

Tuesday, November 30, 2021

AN GINA BURTSATSE GOMA A SASSAN HADEJIA..

 30 November 2021. 



Shugaban karamar hukumar hadejia Hon Abdulkadir Bala Umar T.O. Ya kammala aikin tona Sabbin Burtsatse (Tuka tuka) guda Goma a sassa daban daban na karamar Hukumar hadejia. 

Shugaban Karamar hukumar hadejia Honourable Bala Umar T.O. ya bayyana wannan aiki a matsayin wata hanya ce ta rage wahalar rashin ruwan sha a sassan da aka gina, sannan ya shawarci mazauna unguwannin da aka gina wannan Burtsatse da su rinka kula wajen sanarwa masu Unguwanni in ya lalace don gyarawa. 

Shugaban ya bayyana dalilin samo Wannan aikin a bisa kauracewa shiga karancin ruwa a wurare da dama na karamar hukumar, Kuma Alhamdulillah Masu unguwanni da wakilan Alumma da kungiyoyin Unguwanni sun nuna farin cikinsu da godiyarsu ga jajirtatten jagora A matsayin Shugaban karamar Hukuma. Tun zaman sa shugaban karamar hukumar Hadejia, Alhaji Bala Umar ya dukufa wajen inganta rayuwar Al'ummar wannan yanki, bayan ayyuka na raya karkara shugaban ya samar da wani tsari na tallafawa Mata masu kananan sana'oi wadda ake shirin kaddamarwa nan ba da jimawa ba. 

Daga karshe ya shawarci Alumma cewa suzama wakilan kansu wurin kula da wannan cigaba, yadda za'a jima Ana mora.


Daga Salisu Sogi Hadejia. 

Chairman Media Aide.

Monday, November 29, 2021

AN KADDAMAR DA GYARAN IDO KYAUTA A JIHAR JIGAWA...



Daga Garba Tela Hadejia... 

ƘUNGIYAR MATASA MUSULMAI TA DUNIYA DA GWAMNATIN JIHAR JIGAWA DA HAƊIN GWIWAR GIDAUNIYAR MALAM INUWA SUN ƘADDAMAR DA AIKIN GYARAN IDO KYAUTA:-

A  satin da ya gabata, ɗumbin mutane masu fama da lalurar matsalar Ido kimanin mutum ɗari bakwai da ashirin da tara, (729) ne su ka amfana da samun aikin gyaran ido, da gilashin ƙara ƙarfin gani a fagen karatu, haɗi kuma da magungunan ciwon ido kyauta a Jihar Jigawa. 

Ƙungiyar musulmai matasa ta Duniya, da gwamnatin Jihar Jigawa, da haɗin gwiwar Gidauniyar ba da agaji ta Malam Inuwa, (Malm Inuwa Foundation) su ne su ka ɗaukin nauyin gudanar da aikin, su ka kuma ƙaddamar da shi a wannan rana a babbar Asibitin Kwanciya ta Haɗejia, (Haɗejia General Hospital), inda ɗumbin al'mma daga sassa daban-daban na Jihar Jigawa su ka je aka yi musu aikin kyauta.

A cikin waɗannan jimillar mutanen kimanin (729), kimanin mutane hamsin ne aka yi wa aikin gyaran ido, aka kuma ba su magunguna kyauta, (Free Cataract Surgery, 50 Patient).

Sai kuma kimanin mutune ɗari biyu da ashirin da tara, waɗanda aka rabawa Gilashin ƙara ƙarfin gani domin samun damar karatu garau, (Free Dispensing Of Glasses, 229 Patient).

Sannan, kimanin mutum ɗari huɗu da hamsin ne aka rabawa magunguna kyauta bayan binciken likitoci ya tabbatar da matsalarsu ba ta gilashi ba ce, ba kuma ta aiki ba ce, magani kawai su ke buƙata lafiyar idonsu ta farfaɗo, 

(Free Drugs And Treatment, 450 Patients).

Ɗaya daga cikin marasa lafiyan da ya amfana da wannan aikin gyaran ido kyauta a zantawar da na yi da shi, ya shaida min cewa ya shafe tsawon shekara guda ya na fama da lalurar ido amma bai samu damar neman magani ba sai a wannan lokaci ya samu an yi masa aiki kyauta.

Ɗumbin marasa lafiyar da su ka amfana da wannan tallafi da al'umma gabaɗaya sun bayyana farin cikinsu da jin daɗinsu kan wannan aikin ido kyauta, sun kuma yi addu'ar fatan alkhairi ga wannan ƙungiya ta matasa musulmai ta duniya, da kuma gwamnatin Jihar Jigawa, ƙarƙashin jagorancin mai girma gwamna, Alhaji Muhammad Badaru Abubakar, (MON, MNI), da gidauniyar Malam Inuwa, da wanda ya assasa gidauniyar, mai girma shugaba hukumar bunƙasa fasahar sadarwar zamani ta ƙasa, (NITDA), Malam Kashif Inuwa Abdullahi, (CCIE) bisa wannan agaji da su ka yi. 

Aikin na gyaran ido kyauta wanda aka ƙaddamar da fara aiwatar da shi a yau, za a shafe tsawon kwanaki huɗu ana gudanar da shi, inda za a kammala a ranar Laraba, 24 ga wannan wata na Nuwamba, 2021. Insha Allah.



Sunday, July 3, 2016

AL'ADUN KASAR HADEJIA.... Kashi na Daya (1)



WASU DAGA CIKIN AL’ADUNMU KYAWAWA…
Kasar Hadejia mutanen cikinta suna da Al’adunsu kyawawa wadda suka dace da koyarwar Addinin musulunci, wadannan Al’adu saboda kyawunsu yasa mun taso a cikin kyakkyawan tsari da taimakon Junanmu. Shekaru da dama da suka gabata zakaga mutumin Hadejia bubba da yaro yana da Tarbiyyar idan yaga bubban mutum ya gaidashi, kokuma idan yaganshi da kaya a hannu yaje ya karveshi, wannan Al’ada tana da kyau kuma tayi daidai da tsarin Addinin musulunci. Sannan a shekarun baya duk Unguwar da kaje zakaga tsarin zamantakewarsu akwai ban sha’awa, domin wurin zaman manya daban na yara daban sannan idan zaka wuce Bubban mutum yana zaune zaka cire Takalmi sai ka wuce sannan ka saka. Wani abin ban sha’awa shine Lokacin cin Abinci babu yadda zakaga mutum yaci abinci shi kadai ai haduwa ake mutum huxu ko biyar ake ci tare domin neman Albarka. Wannan ya nuna akwai son juna a tsakaninmu, domin wadda Allah bai bashi ikon yin abinci a gidansa ba to bazai wuni da yunwa ba domin idan yazo Dandali zaici tare da ‘yan-uwansa. Haka yara matasa suma kowa yakan dauko abinci daga gidansu a fito a hadu a ci, wannan muke kira da suna Ciyayya.

ZAMANTAKEWA…
Zamantakewa wata kalma ce da take nuni ga yanayin yadda mutum yake rayuwarsa tare da Abokan zamansa wadda Allah ya hadasu, walau a zaman Makwaftaka ko sana’a da sauransu.

TSARIN SHUGABANCHI…
Shugabanci yana nufin rikon on ragamar Al’umma da basu Umarni da kuma yi musu Jagoranci bisa tafarkin da suka aminta dashi, sannan da tsara musu Dokoki da sasanta tsakaninsu. A Kasar Hadejia tsarin shugabanci ya faro ne tun daga cikin gida inda mutum a gidansa shine shugaba mai shirya komai da kuma bada Doka da Oda, sannan sai shugabancin Unguwa wadda ya kasance kowace Unguwa tana da nata shugaban mai sawa da hanawa da bada umarni shine muke kiransa da suna Mai-unguwa. Duk wani umarni yana fitowa ne daga bakin Mai-unguwa kamar hani da kuma sawa. Shi wannan Mai-unguwa duk abinda ya shafi Unguwarsa shine keda iko akai, kamar Umarni, hani, sasanto tsakanin mutane. Kuma duk Bakon da yazo wannan Unguwa akan kaishi gidan Mai-unguwa ne domin shike da Alhakin yaji abinda ke tafe dashi idan mazauni ne shine da hakkin bashi masauki ta haka ake tsaftace Nagari da Mugu a cikin Unguwa. Baya da Mai-unguwa a gari akwai Malami wadda idan wani Bakon malami yazo wurin Wannan malamin za’a kaishi shi zai bashi masauki sannan yaji Dalilin abinda ke tafe dashi. Haka kuma Idan Bakon dan kasuwa ne akan kaishi Gidan Zangoma wadda shine da hakkin saukar Baki musammam masu saye da sayarwa, shi zangoma shine zai tambayeshi irin Hajojin da yake sayarwa kokuma yake saye domin ya sadashi da masu ciniki. Kaga duk wannan yana nuna muna da kyakkyawan tsari na zamantakewa wadda duk mutumin da ya shigo kasar Hadejia ansan Dalilin zuwansa da kuma abinda yazo yi. A duk lokacin da aka samu hakan shi Mai-unguwa shike da Alhakin sanarwa Bulama sannan Bulama ya sanarda Hakiminsa, shi kuma Hakimi zai sanarda Majalissar Sarki.

Wannan tsarin shugabanci shi ake amfani dashi a kasar Hadejia har lokacin zuwan Turawan Mulkin Mallaka. Koda yake Turawa ma da sukazo sai suka lura cewa muna da kyakkyawan tsari na shugabanci, dan haka sai suka nemi Hadin kan Sarakunanmu ya zamanto zasu bada Umarni ne ga Sarakuna sannan Sarakuna su bada Umarni ga Talakawansu. Turawa sunzo sun samemu da Al’adunmu kyawawa sannan muna da tsari na shugabanci kamar yadda Addinin Musulunci ya tanada mana, wannan dalili yasa Turawa suka samu damar Mulkarmu ba tare da sunsha wahala ba.

AL'ADUN KASAR HADEJIA.... Kashi na Daya (1)



WASU DAGA CIKIN AL’ADUNMU KYAWAWA…
Kasar Hadejia mutanen cikinta suna da Al’adunsu kyawawa wadda suka dace da koyarwar Addinin musulunci, wadannan Al’adu saboda kyawunsu yasa mun taso a cikin kyakkyawan tsari da taimakon Junanmu. Shekaru da dama da suka gabata zakaga mutumin Hadejia bubba da yaro yana da Tarbiyyar idan yaga bubban mutum ya gaidashi, kokuma idan yaganshi da kaya a hannu yaje ya karveshi, wannan Al’ada tana da kyau kuma tayi daidai da tsarin Addinin musulunci. Sannan a shekarun baya duk Unguwar da kaje zakaga tsarin zamantakewarsu akwai ban sha’awa, domin wurin zaman manya daban na yara daban sannan idan zaka wuce Bubban mutum yana zaune zaka cire Takalmi sai ka wuce sannan ka saka. Wani abin ban sha’awa shine Lokacin cin Abinci babu yadda zakaga mutum yaci abinci shi kadai ai haduwa ake mutum huxu ko biyar ake ci tare domin neman Albarka. Wannan ya nuna akwai son juna a tsakaninmu, domin wadda Allah bai bashi ikon yin abinci a gidansa ba to bazai wuni da yunwa ba domin idan yazo Dandali zaici tare da ‘yan-uwansa. Haka yara matasa suma kowa yakan dauko abinci daga gidansu a fito a hadu a ci, wannan muke kira da suna Ciyayya.

ZAMANTAKEWA…
Zamantakewa wata kalma ce da take nuni ga yanayin yadda mutum yake rayuwarsa tare da Abokan zamansa wadda Allah ya hadasu, walau a zaman Makwaftaka ko sana’a da sauransu.

TSARIN SHUGABANCHI…
Shugabanci yana nufin rikon on ragamar Al’umma da basu Umarni da kuma yi musu Jagoranci bisa tafarkin da suka aminta dashi, sannan da tsara musu Dokoki da sasanta tsakaninsu. A Kasar Hadejia tsarin shugabanci ya faro ne tun daga cikin gida inda mutum a gidansa shine shugaba mai shirya komai da kuma bada Doka da Oda, sannan sai shugabancin Unguwa wadda ya kasance kowace Unguwa tana da nata shugaban mai sawa da hanawa da bada umarni shine muke kiransa da suna Mai-unguwa. Duk wani umarni yana fitowa ne daga bakin Mai-unguwa kamar hani da kuma sawa. Shi wannan Mai-unguwa duk abinda ya shafi Unguwarsa shine keda iko akai, kamar Umarni, hani, sasanto tsakanin mutane. Kuma duk Bakon da yazo wannan Unguwa akan kaishi gidan Mai-unguwa ne domin shike da Alhakin yaji abinda ke tafe dashi idan mazauni ne shine da hakkin bashi masauki ta haka ake tsaftace Nagari da Mugu a cikin Unguwa. Baya da Mai-unguwa a gari akwai Malami wadda idan wani Bakon malami yazo wurin Wannan malamin za’a kaishi shi zai bashi masauki sannan yaji Dalilin abinda ke tafe dashi. Haka kuma Idan Bakon dan kasuwa ne akan kaishi Gidan Zangoma wadda shine da hakkin saukar Baki musammam masu saye da sayarwa, shi zangoma shine zai tambayeshi irin Hajojin da yake sayarwa kokuma yake saye domin ya sadashi da masu ciniki. Kaga duk wannan yana nuna muna da kyakkyawan tsari na zamantakewa wadda duk mutumin da ya shigo kasar Hadejia ansan Dalilin zuwansa da kuma abinda yazo yi. A duk lokacin da aka samu hakan shi Mai-unguwa shike da Alhakin sanarwa Bulama sannan Bulama ya sanarda Hakiminsa, shi kuma Hakimi zai sanarda Majalissar Sarki.

Wannan tsarin shugabanci shi ake amfani dashi a kasar Hadejia har lokacin zuwan Turawan Mulkin Mallaka. Koda yake Turawa ma da sukazo sai suka lura cewa muna da kyakkyawan tsari na shugabanci, dan haka sai suka nemi Hadin kan Sarakunanmu ya zamanto zasu bada Umarni ne ga Sarakuna sannan Sarakuna su bada Umarni ga Talakawansu. Turawa sunzo sun samemu da Al’adunmu kyawawa sannan muna da tsari na shugabanci kamar yadda Addinin Musulunci ya tanada mana, wannan dalili yasa Turawa suka samu damar Mulkarmu ba tare da sunsha wahala ba.

AL'ADUN KASAR HADEJIA... Kashi na Daya (1)



WASU DAGA CIKIN AL’ADUNMU KYAWAWA…
Kasar Hadejia mutanen cikinta suna da Al’adunsu kyawawa wadda suka dace da koyarwar Addinin musulunci, wadannan Al’adu saboda kyawunsu yasa mun taso a cikin kyakkyawan tsari da taimakon Junanmu. Shekaru da dama da suka gabata zakaga mutumin Hadejia bubba da yaro yana da Tarbiyyar idan yaga bubban mutum ya gaidashi, kokuma idan yaganshi da kaya a hannu yaje ya karveshi, wannan Al’ada tana da kyau kuma tayi daidai da tsarin Addinin musulunci. Sannan a shekarun baya duk Unguwar da kaje zakaga tsarin zamantakewarsu akwai ban sha’awa, domin wurin zaman manya daban na yara daban sannan idan zaka wuce Bubban mutum yana zaune zaka cire Takalmi sai ka wuce sannan ka saka. Wani abin ban sha’awa shine Lokacin cin Abinci babu yadda zakaga mutum yaci abinci shi kadai ai haduwa ake mutum huxu ko biyar ake ci tare domin neman Albarka. Wannan ya nuna akwai son juna a tsakaninmu, domin wadda Allah bai bashi ikon yin abinci a gidansa ba to bazai wuni da yunwa ba domin idan yazo Dandali zaici tare da ‘yan-uwansa. Haka yara matasa suma kowa yakan dauko abinci daga gidansu a fito a hadu a ci, wannan muke kira da suna Ciyayya.

ZAMANTAKEWA…
Zamantakewa wata kalma ce da take nuni ga yanayin yadda mutum yake rayuwarsa tare da Abokan zamansa wadda Allah ya hadasu, walau a zaman Makwaftaka ko sana’a da sauransu.

TSARIN SHUGABANCHI…
Shugabanci yana nufin rikon on ragamar Al’umma da basu Umarni da kuma yi musu Jagoranci bisa tafarkin da suka aminta dashi, sannan da tsara musu Dokoki da sasanta tsakaninsu. A Kasar Hadejia tsarin shugabanci ya faro ne tun daga cikin gida inda mutum a gidansa shine shugaba mai shirya komai da kuma bada Doka da Oda, sannan sai shugabancin Unguwa wadda ya kasance kowace Unguwa tana da nata shugaban mai sawa da hanawa da bada umarni shine muke kiransa da suna Mai-unguwa. Duk wani umarni yana fitowa ne daga bakin Mai-unguwa kamar hani da kuma sawa. Shi wannan Mai-unguwa duk abinda ya shafi Unguwarsa shine keda iko akai, kamar Umarni, hani, sasanto tsakanin mutane. Kuma duk Bakon da yazo wannan Unguwa akan kaishi gidan Mai-unguwa ne domin shike da Alhakin yaji abinda ke tafe dashi idan mazauni ne shine da hakkin bashi masauki ta haka ake tsaftace Nagari da Mugu a cikin Unguwa. Baya da Mai-unguwa a gari akwai Malami wadda idan wani Bakon malami yazo wurin Wannan malamin za’a kaishi shi zai bashi masauki sannan yaji Dalilin abinda ke tafe dashi. Haka kuma Idan Bakon dan kasuwa ne akan kaishi Gidan Zangoma wadda shine da hakkin saukar Baki musammam masu saye da sayarwa, shi zangoma shine zai tambayeshi irin Hajojin da yake sayarwa kokuma yake saye domin ya sadashi da masu ciniki. Kaga duk wannan yana nuna muna da kyakkyawan tsari na zamantakewa wadda duk mutumin da ya shigo kasar Hadejia ansan Dalilin zuwansa da kuma abinda yazo yi. A duk lokacin da aka samu hakan shi Mai-unguwa shike da Alhakin sanarwa Bulama sannan Bulama ya sanarda Hakiminsa, shi kuma Hakimi zai sanarda Majalissar Sarki.

Wannan tsarin shugabanci shi ake amfani dashi a kasar Hadejia har lokacin zuwan Turawan Mulkin Mallaka. Koda yake Turawa ma da sukazo sai suka lura cewa muna da kyakkyawan tsari na shugabanci, dan haka sai suka nemi Hadin kan Sarakunanmu ya zamanto zasu bada Umarni ne ga Sarakuna sannan Sarakuna su bada Umarni ga Talakawansu. Turawa sunzo sun samemu da Al’adunmu kyawawa sannan muna da tsari na shugabanci kamar yadda Addinin Musulunci ya tanada mana, wannan dalili yasa Turawa suka samu damar Mulkarmu ba tare da sunsha wahala ba.

Friday, February 26, 2016

JIGAWA ENPOWERMENT NEWS....




The Jigawa State Government has today empowered a unit of okada riders with 41 units of Qlink 150 motor cycles which are to be used for commercial purposes.
The total cost of the motor cycles is N6,285,000.00K, which the Government subsidized 35% on cost to the unit whom are to pay 65% on cost back to the Government coppers in 66 weeks.

The motor cycles were distributed by the Special Assistant on Economic Empowerment Muhammad Sheikh Mujaddadi together with personnel of the Directorate of Economic Empowerment to the beneficiaries.

The S A on behalf of the state Government called on the group to utilize the motor cycles and repay the Government back as scheduled and agreed upon so that others will benefit with the revolving loan.
Long live Jigawa State, long live Fed Rep of Nigeria and long live G MB Abubakar ( Badrul Deenal Islam ) the pride of the future generation.

posted from Bloggeroid

KUNGIYAR HADEJIA INA MAFITA TA KARBI BAKUNCIN KUNGIYAR JIGAWA NORTON WEST..

Daga Nasiru Kainuwa Hadejia.  Ziyarar wakilai da ga gamayyar ƙungiyoyin masarautar Ringim, zuwa ga ƙungiyar Hadejia Ina Mafita Initiative a ...