Wannan Dandali zai rinka kawo muku Labarai da suka shafi Gwamnatin Jihar Jigawa, da sauran muhimman labarai wadanda suka shafi rayuwar Al'ummah.
Thursday, June 21, 2012
Saturday, June 16, 2012
Friday, June 15, 2012
MAJALISSA TA DAKATAR DA HON.FARUK LAWAN
A yau juma'a ne majalissar Wakilan Nigeria
tayi wani zaman Gaggawa inda ta Bayyana
dakatar da Hon. Faruk Lawan A Mukaminsa
na Shugaban kwamitin binciko badakalar
rarar man fetur. wannan ya biyo baya ne
Inda ake zarginsa da karbar Na goro
kimanin Dala milyan dari uku. Kuma
majalissar tuni ta maye gurbinsa da John
Enoh mai wakiltar Obubra dake Jihar Cross
River. Sannan majalissar ta umarci komitin
ladabtarwa da ya hukunta Secretaren
komitin wato Mr. Boniface Emalo wanda tuni
shima aka rabashi da mukaminsa. kuma
majalissar ta sake duba Matsayar da ta
dauka a ranar 24 ga Afrilu na wanke
kamfanin Zenon daga badakalar tallafin
man. Inda kuma tana nan tana duba
wannan batun.
Thursday, June 14, 2012
JIHAR BORNO
MANYAN BORNO SUN ROKI DA A
KAWO KARSHEN RIKICIN BOKO
HARAM
HADEJIA A YAU! Al'ummar Jihar Borno dake
Arewacin Nigeria sun Roki 'yan kungiyar
Jama'atu Ahlussunna lidda'awati wal jihad
wadda aka fi sani da suna Boko Haram da
su Amince a tattauna dasu da Gwamnati
domin a kawo karshen Hare harenda yake
janyo Rasa rayuka da gidaje. A wata fira da
yayi da 'yan jarida a Maiduguri Dr. shettima
Ali Munguno ya bayyana rikicin boko haram
a matsayin rikici ne wanda ya janyo Asarar
rayukan Al'umma da gidaje, kuma ya janyo
Rashin aikin yi ga Al'umma. Ya bayyana
cewa mutane basu kwanciyar hankalin da
zasu tafiyar da rayuwarsu a tsinake, ko
harkokinsu na yau da kullum.uma ya
bayyana cewa Jama'a basu samun salloli
Biyar a cikin Jam'i saboda fargabar abinda
zai kasance,Saidai mutum yayi sallarsa a
cikin gidansa saboda rashin samun
nutsuwa. Dr.Ali Munguno ya kara da cewa
yana rokonsu da su Amince a tattauna dasu
domin a kawo karshen Asarar rayuka da
ake. yace a matsayinsu na 'yan kasa suna da
ikon rayuwa a jikin mutane ba tare da
tsangwama ba. yace duka mu da su
kasarmu ce, bamu da wata kasar da tafi
wannan. kuma ya kara da cewa Gwamnatin
tarayya tare da gwamnatin Jiha a hada
hannu wajen tattaunawar domin a kawo
karshen wannan Al'amari. http://
Isabohadejia.blogspot.com/
TARIHIN SARKI HARU BUBBA
TARIHIN SARKIN HADEJIA HARU
BUBBA
Sarkin Hadeji Haru bubba shine Mahaifin
Sarkin Hadejia Muhammadu mai Shahada,
wanda a zamaninsa Turawa sukaci Hadejia
da yaki. Sarki Haru bubba Malami ne kuma
mutum ne mai son zaman lafiya, kuma shine
ya gina Masallacin juma'a Na Hadejia. Kuma a
zamaninsa Gumel sukayi yaki da Hadejia,
wato lokacin sarkin Gumel Abdu jatau.
Sarkin Gumel ya aikowa Sarkin Hadejia zai
wuce ta kasarsa wato ta kudu a gayawa
Talakawa kada su tsorata bazai taba kowa
ba. To amma koda yazo wucewa sai ya saba
Alkawari don yana sawa ana debe kayan
talakawan ana kaiwa Gumel. Koda Sarkin
Hadejia ya samu labari sai yasa akayi sirdi
aka fita, a wannan yakin aka kashe sarkin
Gumel Abdu jatau. Galadiman Hadejia
yakuba shine ya sareshi. Dama sarkin Gumel
yayi mafarki bazai koma gida ba. Sai ya
fadawa kaninsa Abubakar in ya mutu to a
kaishi Gumel ayi masa jana'iza, kuma hakan
akayi. Kuma a zamanin Sarkin Hadejia Haru
ne Dansa Muhammadu Yayi yaki da
Maguzawan Mada Rumfa ta Sokoto, inda
sarkin musulmi ya masa sarautar Sarkin
yakin Sarkin Musulmi. Kafin ya Zama Sarkin
Hadejia. Allah yaji kansu.
Wednesday, June 13, 2012
TARIHIN SARAUTAR FULANI A
HADEJIA! A TAKAICE.
HADEJIA A YAU!
JIYA NA KAWO MUKU TAKAICACCEN TARIHIN
HADEJIA DA DALILIN KAFUWARTA.
TARIHIN FULANI- BISMILLAHIR-RAHMANIR-
RAHEEM.
Kamar yanda na fada a baya Sarkin Hadejia
Na sarakunan Habe shi ya nada Umaru a
matsayin sarkin fulanin Hadejia, To su fulani
sun taso ne daga Gabas da Machina akan
Hanyarsu ta yin kiwo, ko da sukazo Hadejia
sai suka tadda Garin akwai albarkar kiwo da
noma. Hakan ce tasa suka nemi izni a basu
gurinda zasu zauna A zamanin sarki
Abubakar Sarki na karshe a sarautar HABE.
Kuma suna tafe ne a karkashin jagorancin
HARDO ABDURE DAN JAMDOJI MACHINA. A
lokacin da Umaru yake a matsayin sarkin
fulanin Hadejia sai ya samu labarin jihadin
da SHEHU USMANU DAN FODIYO yakeyi hakan
tasa ya tashi 'yan-uwansa biyu(2) suje suyi
mubaya'a a gun SHEHU. Wato SAMBO DA
LARAIMA kuma hakan sukayi Inda shehu ya
basu Tutar jaddada Addinin Musulunci.
Kuma ya umarci SAMBO ya tsaya a HADEJIA
Shi kuma LARAIMA a MARMA. Saboda can
akwai dauloli suma masu zaman kansu yayi
kokarin Hadesu karkashin Daula guda daya.
kamar DAWA FAGI GATURWA DA MARMA. Shi
kuma SAMBO yaci gaba da jaddada Addinin
Musulunci a HADEJIA DA AUYO DA SAURAN
DAULOLIN SARAKUNAN HABE A karkashin
jagorancin Dan-uwansa Umaru. Bayan
rasuwar sarkin fulani Umaru SAMBO yaci
gaba da jaddada Addinin Musulunci har
saida suka kawar da SARAKUNAN HABE.
Amma ba yaki akayi ba Sai suka Koma Fantai
anan sukaci gaba da rayuwa. (wato akwai
wata tsangaya a kusa da gidan Labaran
fantai nan ne suka zauna) wadansu kuma
suka zauna a Dalla (akwai wata duriya a
dallah har zuwa Library anan suka zauna).
Sarakunan fulani sun karbi mulkin Kasar
Hadejia a karkashinDaular Usmaniyya.
ZAN KAWO MUKU TSARE TSAREN SARAUTA DA
KUMA HAKIMAN WAJEN KASAR HADEJIA A
LOKACIN SARKIN FULANIN HADEJIA MALAM
SAMBO. HADEJIA A YAU!
SARKIN MARMA MUHAMMADU DA
MADARUMFA
HADEJIA A YAU! Kamar yanda kuka gani A
sama Zamu kawo muku Tarihin Zuwan
Sarkin Marma Muhammadu Madarumfa.
Iyakar sokoto da Niger da kuma yakin da
akayi tsakanin Muhammadu da Tigarawan
Madarumfa. akan kogin da ya raba Niger da
Nigeria, kusa da Jibya. A zamanin Sarkin
Musulmi Abubakar Atiku Na Biyu. Kuma
zamu baku tarihin Sarautarsa ta Sarkin yakin
Sarkin Musulmi da kuma dawowarsa Hadejia
da yanda aka kaiwa Sarkin Hadejia Haru
Bubba Labarin Muhammadu. Harda Asalin
Jafi da ake Ran sallah A kusa da Masallacin
Juma'a. Muhammadu na Allah Ruwan kogi
Tafi sannu sannu Wanda yayi wargi Ya
Halaka. Giwa ta gama da Masu Karfi Ta wuce.
HADEJIA A YAU
The Government and Society of Hadejia in
the 19th Century:
The government of Hadejia in the 19th
century, like other emirates of the old
Sokoto Caliphate, was based on autocracy.
The emir who was a spiritual as well as
temporal head was at the helm of affairs. He
was assisted in governing by a class of
officials or titleholders who were resident in
his court. It was only the Sarkin Auyo who
was permitted to stay outside the
headquarters: he lived permanently at Auyo
town. The composition of these titIe holders
or Hakimai was made up of 'ya'yan Sarki
(Princes), Dangin Sarki (emir's relatives),
Barorin Sarki (clients), and Bayin Sarki
(slaves). The structure of this emirate's
administration was never dominated by the
"Fulani ruling caste", since the
heterogeneous nature of the area was
taken into cognisance in the distribution of
both civil and military offices. For example,
during Sambo's reign the title of Madaki was
held by a Bamange and that of Galadima
was given to a Ba-Auyaki, both non-Fulani
tribes.
Militarily, the emir was the Commander-in-
Chief of the emirate, delegating his function
in practice to Sarkin Yaki (Captain General or
War Chief), Jarma (Chief of the Brave Ones),
Madaki, Sarkin Arewa and other war chiefs.
The composition of the entire military force
was made up of courtiers, title-holders and
their household slaves, Dogarai (the
emirate's bodyguards) and contingents
from the "fiefs". Hadejia had two broad
sectors of the army: the cavalry (Barade) and
foot soldiers. Militarily the emirate was
considered to be the strongest emirate east
of Kano. This reputation it enjoyed and
enhanced right from the days of the Buhari
Revolt up to the coming of the British.
Subscribe to:
Posts (Atom)
KUNGIYAR HADEJIA INA MAFITA TA KARBI BAKUNCIN KUNGIYAR JIGAWA NORTON WEST..
Daga Nasiru Kainuwa Hadejia. Ziyarar wakilai da ga gamayyar ƙungiyoyin masarautar Ringim, zuwa ga ƙungiyar Hadejia Ina Mafita Initiative a ...
-
Daga Nasiru Kainuwa Hadejia. Ziyarar wakilai da ga gamayyar ƙungiyoyin masarautar Ringim, zuwa ga ƙungiyar Hadejia Ina Mafita Initiative a ...
-
HADEJIA A YAU! Kasar Hadejia tana da kabilu da dama wadanda kuma suke da yarensu daban-daban: kamar 1,HAUSAWA 2, ABORAWA (FULANI) 3, MANGAWA...
-
SARDAUNA/SHATIMA SUN KARBI RANTSUWAR KAMA AIKI.... Daga Garba Tela Hadejia. A yau juma'a 29-5-2015 ne sabon zababben gwamnan jihar...