Wednesday, October 31, 2012

HADEJIA A YAU!: TAKAICACCEN TARIHIN LIMAMIN HADEJIA M. YUSUF IMAM....

HADEJIA A YAU!: TAKAICACCEN TARIHIN LIMAMIN HADEJIA M. YUSUF IMAM....: Free Music Free Music Hadejia A yau. A ci gaba da kawo muku Tarihin wadanda suka bada Gudunmawa a Hadejia, yau Zamu baku takaitaccen Tarihi...

HADEJIA A YAU!

Monday, October 29, 2012

HADEJIA A YAU!: TARIHIN KAFUWAR HADEJIA KASHI NA (1)

HADEJIA A YAU!: TARIHIN KAFUWAR HADEJIA KASHI NA (1): HADEJIA- TARIHIN KAFUWAR Hadejia Ya farune daga wani maharbi mai suna Hade, a yawon farauta da yakeyi ne wata rana yana tafe da karyar sa s...

HADEJIA A YAU!

Monday, October 22, 2012

KWANAKIN HAJJI DA WURARE GOMA MASU ALBARKA. DAGA M. AMINU DAURAWA.

Easily Upload Your Images To Myspace
Free Music Hadejia a yau. Na daya ranar takwas ga watan hajji, sunanta
yaumuttarwiyya,
shine alhazai suke zuwa mina su wuni su kwana,
Na biyu ranar tara ga wata itace ranar arfa, itace
alhazai suke wuni a
filin arfa zuwa faduwar rana, daganan su tafi
Muzdalifa su kwana
Na uku ranar goma ga wata, itace alhazai suke
gabatar da aiyuka
guda biyar a cikinta, jifa, yanka, aski, dawafi, saayi,
Na hudu ranar sha daya , da sha biyu, da sha uku,
sune ranakun
kwanan mina da jifa, Abubuwa goma masu daraja a
Macca
wadanda suke da alaka da aikin hajji, wadanda ake
aiwatar da aikin
hajji, daura da su sune, na daya, Ka'aba ana kewaya
ta sau bakwai,
na biyu, alhiji (wanda ake cewa hijri isma'ila) ana
shiga ciki ayi
salla,daidai yake da yin sallah a cikin Ka'abah, na uku,
makamu
ibrahim, wanda ake sallah Raka'a biyu a bayansa
bayan gama
dawafi, na hudu, Alhajrul'aswad, (dutsen aljannah)
ana sunbatarsa
(kiss) a shefeshi, ayi sujjada akansa, ko anunashi daga
nesa ayi
kabbara, na biyar ruwan zamzam, ana sha a shafa a
fuska, a zuba
ajiki, ayi addu'a, aroki Allah bukarar duniya da lahira
hadisi ya
tabbata, akan haka, na shida Dutsen safa da marwa,
wanda ake
zirga-zirga tsakanin su sau bakwai a fara daga sama a
kare a marwa,
na takwas, mina wajen kwana da ranakun jifa, na tara
arfa da
muzdalifa, a wuni a arfa a kwana a muzdalifa, na
goma wajen jifa
guda uku, inda ake jefa tsakuwa guda saba'in, Allah
ta'ala yace
wanda ya girmama alamomin addinin Allah, yana
daga cikin tsoran
Allah na zuci, wanda duk yayi sallah a masallacin
macca yana da
lada dubu dari, wanda ladan ya shafi dukkan fadin
iyakokin harami,
tun daga ka'abah, Manzon Allah saw yace :Duk
wanda yayi hajji,
baiyi kwarkwasaba (maganar batsa da mata) baiyi
fasikanciba, zai
dawo kamar ranarda mahaifiyarsa ta haifeshi, kuma
yace, Hajji
kubutacce(shine wanda akayishi akan sunnah da iklasi
da ilmi) bashi
da sakamako sai aljannah, ku tayamu da addu'a mu
sami wannan
garabasar, Allah ya karbi ibadarmu yasa mu dace da
sunnah da
iklasi na gode

Tuesday, October 9, 2012

Easily Upload Your Images To Myspace
Free Music HADEJIA A YAU!
SARKIN HADEJIA UMARU: A SHEKARAR 1863 allah ya
yiwa Sarkin Hadejia Buhari rasuwa a Yakinsu da sukayi
da Gogaram (bade). Ko da aka dawo Hadejia aka binne
shi sai Manyan fadawan Hadejia wadanda akwai Amana
tsakaninsu dashi Buhari.

Kamar SARKIN AREWA TATA
GANA (GINSAU MAI KINA BAWO) DA KUMA SARKIN
YAKI JAJI suka jajirce Sai an Nada UMARU DAN BUHARI
SARKIN HADEJIA. kuma hakan Akayi!
SARKIN HADEJIA UMARU NA BIYU an nadashi yana da
shekara Goma sha Hudu. Kuma manyan fadawan
Mahaifinsa sune suke gudanar da Sarautar tunda shi
yaro ne. Kuma a zamaninsa Sarkin Damagaram
Tanimu ya kawo yaki Hadejia. Kuma yayi sansani a
Arewa da Hadejia daga nan har Jigawar Kasim
mutanensa ne. saida yayi kwana Arba'in ana yaki
amma Hadejiawa basu fasa wasanninsu na dandali ba.


Wata rana ana yaki Sai aka harbi dokin Sarkin Arewa!
Koda ya mutu sai akaje gida aka dauko wani Dokin aka
cire kayan wancan Dokin aka sakawa wanda aka kawo.
Tata gana ya koma kan doki, kashe gari ana cikin yaki
sai Tata gana ya sauko daga Dokinsa yayi alwala ya
koma kan Dokin, to ashe Sarkin Damagaram yana
kallon su sai yace Lalle Sarkin Hadejia ya Isa ana yaki ka
sauko kayi alwala? Jiya ma an kashe masa Doki amma
saida akaje aka dauko wani a gari? Sai Zagin Sarkin
Damagaram yace ai ba Sarkin Hadejia bane Yaronsa ne!
Sai Sarkin Damagaram Tanimu yace to Ina Sarkin
Hadejian? Sai zaginsa yace ai ance yana gida tunda aka
fara yakin nan bai taba zuwa ba. Sai sarkin Damagaram
yace wa fadawansa Gobe zamu bar Hadejia kar mu
tsaya ayi ta kashemu. Saboda Sarkin Hadejia ya raina
mu kwananmu Arba'in amma bai taba zuwa anyi yaki
dashi ba? Wa yasan me zai mana in ya zo? Amma basu
san Sarkin Yaro bane. Washe gari suka juya suka koma
Damagaram.

Kuma lokacinda sukazo Hadejia Da kaka
ne! Anyi girbi Manoma basu gama Tare Amfaninsu ba.
Shi yasa suka dade a Hadejia saboda akwai abinci da
ruwa a kusa dasu. SARKIN HADEJIA UMARU Mutum ne
mai son Nishadi kowane Lokaci yakan fita Bakin kogi ko
Gona Domin Debe kewa. Kuma anyi amfani da wannan
Damar inda wata rana ya fita sai aka Rufe Masa Kofa.


Koda yazo yaga kofa A rufe sai ya juya ya tafi Chamo
ya zauna. Aka nada Kanin Mahaifinsa Sarkin Hadejia
Wato HARU BUBBA. 1865-1885. Shi kuwa UMARU DAN
BUHARI yayi zamansa a Chamo kuma Ya rasu a
shekarar 1920. Allah yaji Kansu Ameen.
HADEJIA A YAU

HADEJIA A YAU!: KASAR HADEJIA DA KABILUN CIKINTA

HADEJIA A YAU!: KASAR HADEJIA DA KABILUN CIKINTA: HADEJIA A YAU! Kasar Hadejia tana da kabilu da dama wadanda kuma suke da yarensu daban-daban: kamar 1,HAUSAWA 2, ABORAWA (FULANI) 3, MANGAW...

Saturday, October 6, 2012

THE 19TH CENTURY JIHAD AND ESTABLISHMENT OF HADEJIA EMIRATE

Easily Upload Your Images To Myspace
Free MusicHADEJIA A YAU!
The new ideas generated as a result of
their policies had brought together
people of diverse (descent) linguistic
and occupational groups under one
umbrella. Although ever since their
migration into Hausa land, some fulani
Jihadists in due course became
confidants and advisers to some Hausa
rulers, there was a strong and
persistent tendency among the
Jihadists of avoiding close association
with HABE SARAKUNA, either because of
the fear or being contaminated with
Illigally acquired wealth or because
most of the Habe palaces remained a
stronghold of various traditional cults
such as BORI Cult. This made the
devoted Ulamas keep their distance
from the rulers (sarakuna). It was the
relationship between these two classes
the Ulamas and the Habe rulers that
eventually led to the outbreak of the
Jihad in Hausa land at the beginning of
the 19th Century.
The condition of Hausa society at the
eve of Jihad was anything but fair,
especially the socio-economic system.
Virtually all the rulers were norminal
Muslims and therefore hardly enforced
the Sharia system. At the same time
enforced excessive taxation. Yet in the
midst of the suffering and hardship,
the rulers continued to be corrupt,
unjust and indifferent to the plight of
the oppressed.
There seem to be some confusion as
regards the exact time when the fulani
Jihadists first came and established
their wet-season camps in the plentiful
grazing land of the Auyo/Hadejia
riverrine savannah land, the confusion
is due to the multiple causes of
Nomadic Fulani movements in the
Nigerian Savannah in general and the
Hadejia area in particular. H.M. Brice
Smith, has placed the coming of the
Fulani into the Hadejia area at the
middle or late 1700 A.D. But according
to A. Abdu Maigari, the Fulani came to
Hadejia area from Machina in Borno
during the 15th Century.
An early Fulani settler in Hadejia who
became very influential in one Hardo
Abdure dan Jamdoyji, wealthy Fulani
who traced his Origin to Machina in
Borno. Hardo Abdure established his
dry season camp in Hadejia at Jarmari
during the early 18th Century.
Jarmari is located few kilometres from
Hadejia town. As the case will all
Nomadic Fulani camps the one
established by Hardo Abdure at Jarmari
was not meant to be permanent abode.
Rather it was ment to serve the
purpose of their seasonal movements.
HADEJIA A YAU!

Wednesday, September 12, 2012

KASAR HADEJIA DA KABILUN CIKINTA


HADEJIA A YAU! Kasar Hadejia tana da kabilu da dama wadanda kuma suke da yarensu daban-daban: kamar 1,HAUSAWA 2, ABORAWA (FULANI) 3, MANGAWA 4, GIZMAWA 5, BADAWA 6, KOYAMAWA.
1, HAUSAWA:- Kabilar Hausawa sune kabila mafiya yawa a kasar Hadejia Domin su babu wanda zaice ga lokacinda suka shigo Kasar Hadejia. kuma tafi karfi a kasar sakamakon dadewar Garuruwansu. kamar Garun Gabas (Biram), Auyo, da Matsa. kuma ko zuwan Bayajidda Garun Gabas yazo ne ya samu Mutanen Garin suna yin Hausanci.

2, ABORAWA (Fulani):- Kabilar fulani sun shigo kasar Hadejia tun a Farkon karni na goma sha biyar (15) kuma sun shigo ne daga yankin Machina wasu kuma daga Katsina, kuma sun Taho ne daga Gabar Kogin SENEGAMBIA wato SENEGAL.sun fara zama ne a Rinde wasu kuma sun Zauna a Jarmari wasu a Marke wasu a Adiyani da Margadu. Kuma ayarinsu ya kasu biyu Inda wasu suka wuce kasar Kano Karkashin Jagorancin Lamido Usman Kalinwama. A Karni na goma sha Tara (19) Wasu fulanin sun sake shigo Kasar Hadejia daga yankin Machina Karkashin Jagorancin Ardo Abdure Dan Jamdoyi. Kuma ance Kafin suzo Hadejia saida suka zauna a Kankiya ta Jihar Katsina. kuma wadannan fulani suke Sarautar Hadejia har zuwa Yau.
3, MANGAWA:- Kabilar Mangawa ko Barebari wadanda mafi yawancinsu suna zaune a Gabas da Hadejia da kuma Arewacin kasar Sun zo ne A karni na goma sha bakwai (17) sun taho ne daga yankin Borno kuma mafiya yawansu sun zo kasar Hadejia ne Tonon Azurfa da Tagullah. Inda kuma daga baya wasu sun shigo kasar Hadejia A lokacinda RaBe yaci Kukawa da Yaki sai suka kaura suka dawo kasar Hadejia, Kamar Birniwa,Baramusa,Kacallari, da Sauransu.
4, GIZMAWA:- Gizmawa suma kamar Mangawa sun shigo ne a Karni na goma sha bakwai (17) kuma suma suna zaune ne a yankin Guri, Marma, Lafiya da sauransu kuma suma yarensu kusan kamar barbarci ne saidai wasu kalmomin da yake canzawa.
5, BADAWA:- Kabilar Badawa basu da yawa a kasar Hadejia, kuma suna zaune ne a Garuruwan Iyakar Hadejia da Bedde, Kamar Gayin, Adiyani, Margadu,da Kadira. wasu sun zauna anan ne tun kafin yakin Gogaram. wasu kuma sunce dama anan suke tuntuni. ganin cewa suna iyaka ne da Kasar Bedde.
6; KOYAMAWA:- Kabilar koyamawa suma basu da yawa kuma Dangin Barebari ne, sai dai zanensu ya bambanta. kuma yarensu ma ba iri daya bane. Kuma suna cewa sun taho ne daga Gabas da Sudan. sannan suna zaune ne a Kasar Kafin Hausa,Bulangu,Yayari, koyamari da sauran garuruwan kasar Kafin hausa.

7; TIJJANAI:- Kabilar Tijjanai fulani ne dake zaune a Yelleman kuma Malamai ne masu bin Darikar Tijjaniyya. shi yasa ake ce musu Tijjanai. Sun shigo kasar Hadejia a shekarar 1903, Daga Malo a yankin Tukolar Senegal. sun taho ne bayan Turawan France sun yiwa Yankinsu Mulkin Mallaka. sun taho karkashin jagorancin Shugabansu Muhammadu El-Bashir, kuma sun fara zama ne a Lokoja. Magajinsa kuma Ahmadu Madaniyyo sai ya sake tasowa daga Lokoja yazo Kasar Hadejia aka basu Guri suka zauna. wato Yelleman Tijjanai. Alhamdu lillahi. Hadejia A Yau.

Sunday, September 9, 2012

CAPTAIN PHILLIPS MAITUMBI


[London Gazette, 26
June 1902]: "H C B
Phillips, Captain,
Imperial Yeomanry.
In recognition of
services during the
operations in South
Africa". He served in
Northern Nigeria in
1903, and received
the Medal and clasp;
was for some time
Resident, Northern
Nigeria, and died at
Hadeija, Northern
Nigeria, on 1
September 1906. An
obituary notice of
him appeared in the
'The Times', Captain
Phillips had married,
in 1885, H E,
daughter of
Harwood Hoyle, of
Lancashire.
Source: DSO
recipients (VC and
DSO Book)

RUWAN DAMINA A HADEJIA



HADEJIA A YAU! Kamar yanda Aka sani Garin Hadejia Gari ne wanda Allah ya Albarkacemu da Ni'imomi da dama! musamman Kasar Noma da Ruwan kogi wanda kuma muke Alfahari da shi domin Noman Rani,Kifi, da kuma Dajin Kiwon Dabbobi da sauransu. Ko ban fada ba Tarihi ya Nuna cewa Hadejia ta kafu ne sakamakon Ruwa da ya wuce ta kasar Garin. shi kuma Ruwa yana tafe da Albarkatu da Dama kamar yanda na fada a baya! hasali ma Hadejia Ruwa ne ya kewayeta ta ko Ina. kuma muna Alfahari da hakan Saboda tattalin Arzikinmu. kamar yanda aka saba duk Shekara ana Samun Barazana Saboda Cikar Kogi da Gulbi da muke Dasu. A ranar Larabar nan Allah ya Ni'imtamu da Ruwan sama kamar da Bakin Kwarya. wanda kuma yayi Asarar Dukiyoyi da Gidaje da Dama. Muna Taya wadanda wannan Abu ya shafa jaje da kuma Addu'ar Allah ya Maida musu da Alkairi . AMEEN. kuma muna kara jawo Hankalin Mutanenmu da su rinka kula da tsaftace Magudanan Ruwa. sau da dama Idan Damina Ta wuce sai mu maida Magudanan Ruwanmu gurin zuba shara wanda kuma Hakan yana janyo mana Hasarar Gidaje da Dukiya! wani Lokaci ma Harda Rayuka. kowa ya gyara ya sani. Kuma muna kira ga Gwamnati da ta Rinka kula da kyautata Magudanan Ruwanmu, A matsayinta na Mai doka da Oda ko Ince wadda abin ya Shafa. Nasani tana Iya bakin kokarinta Domin mun samu labari wasu ma Tuni Gwamnati ta Jima da basu Sabon Matsuguni Amma Suka ki su tashi. Allah ya saka da Alkairi. Hadejia A yau.

Saturday, September 8, 2012

YAKIN KAFUR KO GAMON KAFUR


HADEJIA A YAU!
Bayan da aka kare Yakin Takoko inda aka kashe Sarkin Hadejia Ahmadu, Daular sokoto dai sunki yarda da Buhari a Matsayin Sarkin Hadejia. Sarkin Musulmi Alu Bubba sai ya gayyaci duk sarakunan dake Karkashin Daular sokoto da su hadu su yaki Buhari. Ko a kamashi da rai ko a kashe shi. Wannan kuwa ta faru ne a shekarar (1853). An hada wannan rundunar yakin ne karkashin Jagorancin Galadiman Kano Abdullahi maje Karofi kafin ya zama Sarkin Kano. An gayyaci mayaka a Garuruwa daban daban kamar Kano,zamfara,Bauchi,Katagum,Misau,zaria da sauran garuruwan Daular Sokoto. Masana tarihi sunce an tara mutum A kalla Dubu Ashirin (20,000) Abdullahi Maje Karofi ya Umarci Sarkin Miga da ya zame musu Jagoran Tafiya, ganin cewa ya fisu sanin Kasar Hadejia saboda Iyakarsu daya. Koda suka shirya sai aka Umarcesu da su shiga Hadejia ta Kudu Maso Yamma, wato kar su shiga kai tsaye ta yamma. Akan Hanyarsu ta zuwa Hadejia ne Sai suka Yada Zango a Kafur, kusa da Hadejia. Domin su kwana da safe su shiga Hadejia su Yaki Sarki Buhari. Sai dai da zuwansu Kafur Buhari ya samu Labari, Ance wani makiyayi ne yana kiwo ya Gansu, kuma Har ya bar gurin baiga Iyakarsu ba. Sai ya rugo ya sanarda Sarki Buhari Abinda ya gani. Sai Buhari ya Umarci Mayakansa cewa "Tunda ance Basu da iyaka kuma ga Magariba ta shigo, mu shirya muje mu shiga cikinsu ba tare da sun ganemu ba" hakan sukayi yace Duk Lokacinda sukaji Dan fatima ya Buga Ganga to su fara Bugun mayaka. Haka akayi Mayakan Buhari suka shimmace su suka shiga cikinsu ba tare da sun gane ba,Saboda Garuruwa da dama ne suka Hadu. Ance wasu mayakan nasu Dauresu akayi wai dan kar su shiga Hadejia kafin Gari ya waye. Ashe Ajali ne ya dauresu.
Koda Sarkin Hadejia Buhari yayi shirinsa yayi Addu'ah sai ya Daga Kai sama. Sai Dan fatima ya zuba Kirari (Fasa maza dan Sambo, Garba Bakin Tandu da Man Madaci, wanda ake jira yazo, fasa Maza gagara gasa, sai ya buga Gangar yaki). Anan Mayakan Hadejia suka fara bugun mayakan Daular Sokoto suna kashewa. Wadansu duk suka razana suka fita a guje kowa yana kokarin ya ceci Ransa. Wadanda aka dauresu dan kar su shiga Hadejia da wuri, duk anan aka kashesu. Sauran kuwa suka zubar Makamansu suka Gudu. Dawakai suka Razana, su kuwa mayakan Hadejia Suna bi suna kashewa suna kama Bayi.

ANNABI MUSA KALAMULLAHI. DAGA IDRIS M. EDDY


ANNABI MUSA(A)
Annabin Allah ne da ya ke magana da Allah
wajen karban sako ba tare da mala'ika a
tsakani ba. Annabi Musa ne Annabin da ya fi
kowanne Annabi shan wahalar isar da
manzanci.
* Na farko ya yi gwagwarmayar neman aure a
Madayyana a gidan Annabi shu'aib
* Na 2 ya yi gwagwarmaya da mutumin da a
tarihi shi kadai ya taba da'awar rububiyya da
uluhiyya. Kuma Allah ya kirashi da gwani
wajen azabtar da mutane. Kuma mutanen sa
na matukar biyayya gare shi kan da'awar sa
ta Allantaka.
* Na 3 ya kai ruwa rana da attajirin da ba a
taba yin irinsa ba a tarihin Duniya. Bayan
wadata ya bijrewa Allah kuma ya sami
tumasawa da jama'ar gari su ka daure mashi
gindi.
* Na 4 ya yi fama da mutumin da a tarihi shi
kadai mala'ika ya rena kuma ya kafirce ya ke
neman kafirtar da jama'ar Annabi
Musa.Samiree ya samar da abin bautar da ba
Allah ba bayan Annabi Musa ya tafi karbo
sakon Allah. Mutane Annabi Musa gaba daya
su ka canja addini sai yan kadan su ka rage.
* Na 5 Annabi Musa ya sha fama wajen
karantar wasu darussa na rayuwa daga
wajen Hadhiru. Bawan Allah n da aka tura
Annabi Musa musamman ya je ya dauko
darasi a wurin shi.
* Na 6 sai famar sa da ta fi kowacce wahala
wacce kuma ita Allah ya fi yawan maimaitawa
a kur'ani kuma ita Allah ke kafawa kafirai
hujja duk lokacin da su ke neman tadawa
wani Annabi hankali kan sai ya kawo masu
hujja,
- Ana sauko masu abinci daga aljanna amma
su ka ce ya ishe su su nomawa za su na yi.
- sun yi laifi ance su nemi gafara da wata
kalma sai su ka canja wata. Kamar ace ku ce
'Gafara' sai su ka ce 'Ga fura'.
- sun ce su sun fasa imanin ma har sai sun ga
Allah da idon su . Aka kai su su ka ji sauti
magana daga Allah suka ce ba su amince ba .
Sai da su ka ga wani haske daga Allah su ka
fadi matatu. Allah ya rayar da su.
- sun tambayi Annabi musa me ya kamata ayi.
Allah ya sanar da shi a yanka saniya. Amma sai
su ka ce wacce iri? Ya fadi irin su ka ce wacce
kala? Sai aka fada musu abin da sai da suka
mika wuya don dole.
- An umarce su da sujjada sun ki sai da aka
sauko da dutse zai fado masu.
- wadannan su ne masu imani daga cikin
mutanensa, amma ko Allah za su kira sai su ce
da Annabi musa ka roka mana Allah nka ya
mana kaza.
* Na 7 Annabi Musa famarsa ta karshe da
mutanesa ce lokacin da Allah ya umarcesu su
shiga gari na karshe da ya rage na al'ummar
Adawa a doron Duniya. Su yaQe su duk da
girmansu su shiga garin su zauna ya zama
nasu mai makon wannan yawo da su ke. Da
yan leken asiri ( su Yusha'u) su ka dawo su ka
bayyana yadda girman Adawa ya ke sai su ka
ce to mu mun tsaya anan ya Musa sai dai in
ku je ku yi yakin da kai da Allah nnaka.
Wannan dalili ya jawo masu dimuwa shekara
40 ba su san inda su ke ba. A wannan
dimuwa Annabi Musa da Annabi Haroon da
dattawa da yawa daga cikinsu su ka rasu.
Annabi (s) ya yi addu'a kan Allah Sakawa
Annabi Musa da alkhairi kan hakuri da ya yi
da cutarwar da jama'arsa su ka masa .
Annabi Musa ne Annabi daya tilo da aka bashi
Annabta kuma ya rokawa dan uwansa
Annabta. Annabi Musa ne aka ambaci sunansa
har x 136 a ckin kur'ani. Annabi Musa suruki
ne na Annabi Shu'aibu(A)
Allah saka wa Hasiya matar Fir'auna da
alkhairi da ta sadaukar da rayuwarta don
amsa da daukaka kiran Annabi Musa.
Allah saka ma Yusha'u da alkhairi saboda
biyayya da bada kwarin gwiwa ga Annabi
Musa da jagorantar rundunar da Annabi Musa
ya mutu ya bari ya je ya cinye garin da yaki su
ka maye garin kamar yadda Allah ya
alkawarta.
Annabi Musa ya taimakawa al'ummar
musulmi da shawartar Annabi(s) da ya nemo
mana saukin sallah daga 50 ta dawo 5 . Allah
kara daraja da gafara ga Annabi Musa(A.s.)

Annabi Musa ya kafa hujja ga kiristoci. Cikin
tsohon alkawari ya na cewa Annabin da zai
zo akarshe kamar ni ya ke, ni ma kamar shi na
ke.
Kamanninsu.
.. Suna da uwa da uba.
.. Sun yi hijra
.. Garinsu da ganuwa
.. Sun yi yaki
.. Sun yi aure
.. Sun haifi yaya
ko nan kamannin su ka tsaya sun wadatar da
cewa a cikin Bible hujja ta tabbata daga
Annabi Musa Annabi Isa ba shine Annabin
karshe ba.

FADAKARWA DAGA MASALLACIN FANTAI. DAGA IDRIS BAFFA


Assalamu Alaikum. Ya yan uwa musulmai, hakika malam husaini
baban(nai‘bin masallacin usman dan fodio dake cikin babbar
sikandiren gwabnati(fantai hadejia) yaja hankalinmu a yayin dake
gabatar da kdabarsa ta sallar juma‘a.malam yayi bayani akan
mahimmacin(ihsa n)kyautatawa, a inda yabukaci mutani su dage
wajen taimakawa masu karamin karfi da kuma taimakawa addinin
musulinci ta bangaruri dabandaban.haki ka malam ya janyo ayuyi
daga AL-QUR‘ANI MAI GIRMA DA KUMA HADISAN MANZO
(SAW)ALLAH MAI GIRMA DA DAUKAKA YAFADA A CIKIN SURA TA
3, AYA TA 91.(Baza ku sami kyautatawaba, sai kun ciyar daga abin
da kukeso. Kuma abin da kuka ciyar, komene ne, to lalle ne ALLAH
gare shi masani ne). Yazo cikin hadisi, wata rana MANZO(SAW) tare
da sahabbansa masu daraja za‘atafi yaki, a wannan lokaci ana cikin
tsanani ga rana, ga sahara ga ba dawakan fita, wasu daga cikin
sahabbai irensu sayyadna ABUBAKAR SIDDIK, UMAR BN KHADDAB
da sauran su. Sun fitar da dukiyoyinsu ba don komaiba sa don
samun rabo mai girma a gobe. Da fatan wannan kudba ta malam
jatayi tasiri cikin zikantamu amin.

Friday, June 15, 2012

MAJALISSA TA DAKATAR DA HON.FARUK LAWAN

A yau juma'a ne majalissar Wakilan Nigeria tayi wani zaman Gaggawa inda ta Bayyana dakatar da Hon. Faruk Lawan A Mukaminsa na Shugaban kwamitin binciko badakalar rarar man fetur. wannan ya biyo baya ne Inda ake zarginsa da karbar Na goro kimanin Dala milyan dari uku. Kuma majalissar tuni ta maye gurbinsa da John Enoh mai wakiltar Obubra dake Jihar Cross River. Sannan majalissar ta umarci komitin ladabtarwa da ya hukunta Secretaren komitin wato Mr. Boniface Emalo wanda tuni shima aka rabashi da mukaminsa. kuma majalissar ta sake duba Matsayar da ta dauka a ranar 24 ga Afrilu na wanke kamfanin Zenon daga badakalar tallafin man. Inda kuma tana nan tana duba wannan batun.

Thursday, June 14, 2012

JIHAR BORNO

MANYAN BORNO SUN ROKI DA A KAWO KARSHEN RIKICIN BOKO HARAM HADEJIA A YAU! Al'ummar Jihar Borno dake Arewacin Nigeria sun Roki 'yan kungiyar Jama'atu Ahlussunna lidda'awati wal jihad wadda aka fi sani da suna Boko Haram da su Amince a tattauna dasu da Gwamnati domin a kawo karshen Hare harenda yake janyo Rasa rayuka da gidaje. A wata fira da yayi da 'yan jarida a Maiduguri Dr. shettima Ali Munguno ya bayyana rikicin boko haram a matsayin rikici ne wanda ya janyo Asarar rayukan Al'umma da gidaje, kuma ya janyo Rashin aikin yi ga Al'umma. Ya bayyana cewa mutane basu kwanciyar hankalin da zasu tafiyar da rayuwarsu a tsinake, ko harkokinsu na yau da kullum.uma ya bayyana cewa Jama'a basu samun salloli Biyar a cikin Jam'i saboda fargabar abinda zai kasance,Saidai mutum yayi sallarsa a cikin gidansa saboda rashin samun nutsuwa. Dr.Ali Munguno ya kara da cewa yana rokonsu da su Amince a tattauna dasu domin a kawo karshen Asarar rayuka da ake. yace a matsayinsu na 'yan kasa suna da ikon rayuwa a jikin mutane ba tare da tsangwama ba. yace duka mu da su kasarmu ce, bamu da wata kasar da tafi wannan. kuma ya kara da cewa Gwamnatin tarayya tare da gwamnatin Jiha a hada hannu wajen tattaunawar domin a kawo karshen wannan Al'amari. http:// Isabohadejia.blogspot.com/

TARIHIN SARKI HARU BUBBA

TARIHIN SARKIN HADEJIA HARU BUBBA Sarkin Hadeji Haru bubba shine Mahaifin Sarkin Hadejia Muhammadu mai Shahada, wanda a zamaninsa Turawa sukaci Hadejia da yaki. Sarki Haru bubba Malami ne kuma mutum ne mai son zaman lafiya, kuma shine ya gina Masallacin juma'a Na Hadejia. Kuma a zamaninsa Gumel sukayi yaki da Hadejia, wato lokacin sarkin Gumel Abdu jatau. Sarkin Gumel ya aikowa Sarkin Hadejia zai wuce ta kasarsa wato ta kudu a gayawa Talakawa kada su tsorata bazai taba kowa ba. To amma koda yazo wucewa sai ya saba Alkawari don yana sawa ana debe kayan talakawan ana kaiwa Gumel. Koda Sarkin Hadejia ya samu labari sai yasa akayi sirdi aka fita, a wannan yakin aka kashe sarkin Gumel Abdu jatau. Galadiman Hadejia yakuba shine ya sareshi. Dama sarkin Gumel yayi mafarki bazai koma gida ba. Sai ya fadawa kaninsa Abubakar in ya mutu to a kaishi Gumel ayi masa jana'iza, kuma hakan akayi. Kuma a zamanin Sarkin Hadejia Haru ne Dansa Muhammadu Yayi yaki da Maguzawan Mada Rumfa ta Sokoto, inda sarkin musulmi ya masa sarautar Sarkin yakin Sarkin Musulmi. Kafin ya Zama Sarkin Hadejia. Allah yaji kansu.

Wednesday, June 13, 2012

TARIHIN SARAUTAR FULANI A HADEJIA! A TAKAICE. HADEJIA A YAU! JIYA NA KAWO MUKU TAKAICACCEN TARIHIN HADEJIA DA DALILIN KAFUWARTA. TARIHIN FULANI- BISMILLAHIR-RAHMANIR- RAHEEM. Kamar yanda na fada a baya Sarkin Hadejia Na sarakunan Habe shi ya nada Umaru a matsayin sarkin fulanin Hadejia, To su fulani sun taso ne daga Gabas da Machina akan Hanyarsu ta yin kiwo, ko da sukazo Hadejia sai suka tadda Garin akwai albarkar kiwo da noma. Hakan ce tasa suka nemi izni a basu gurinda zasu zauna A zamanin sarki Abubakar Sarki na karshe a sarautar HABE. Kuma suna tafe ne a karkashin jagorancin HARDO ABDURE DAN JAMDOJI MACHINA. A lokacin da Umaru yake a matsayin sarkin fulanin Hadejia sai ya samu labarin jihadin da SHEHU USMANU DAN FODIYO yakeyi hakan tasa ya tashi 'yan-uwansa biyu(2) suje suyi mubaya'a a gun SHEHU. Wato SAMBO DA LARAIMA kuma hakan sukayi Inda shehu ya basu Tutar jaddada Addinin Musulunci. Kuma ya umarci SAMBO ya tsaya a HADEJIA Shi kuma LARAIMA a MARMA. Saboda can akwai dauloli suma masu zaman kansu yayi kokarin Hadesu karkashin Daula guda daya. kamar DAWA FAGI GATURWA DA MARMA. Shi kuma SAMBO yaci gaba da jaddada Addinin Musulunci a HADEJIA DA AUYO DA SAURAN DAULOLIN SARAKUNAN HABE A karkashin jagorancin Dan-uwansa Umaru. Bayan rasuwar sarkin fulani Umaru SAMBO yaci gaba da jaddada Addinin Musulunci har saida suka kawar da SARAKUNAN HABE. Amma ba yaki akayi ba Sai suka Koma Fantai anan sukaci gaba da rayuwa. (wato akwai wata tsangaya a kusa da gidan Labaran fantai nan ne suka zauna) wadansu kuma suka zauna a Dalla (akwai wata duriya a dallah har zuwa Library anan suka zauna). Sarakunan fulani sun karbi mulkin Kasar Hadejia a karkashinDaular Usmaniyya. ZAN KAWO MUKU TSARE TSAREN SARAUTA DA KUMA HAKIMAN WAJEN KASAR HADEJIA A LOKACIN SARKIN FULANIN HADEJIA MALAM SAMBO. HADEJIA A YAU!
SARKIN MARMA MUHAMMADU DA MADARUMFA HADEJIA A YAU! Kamar yanda kuka gani A sama Zamu kawo muku Tarihin Zuwan Sarkin Marma Muhammadu Madarumfa. Iyakar sokoto da Niger da kuma yakin da akayi tsakanin Muhammadu da Tigarawan Madarumfa. akan kogin da ya raba Niger da Nigeria, kusa da Jibya. A zamanin Sarkin Musulmi Abubakar Atiku Na Biyu. Kuma zamu baku tarihin Sarautarsa ta Sarkin yakin Sarkin Musulmi da kuma dawowarsa Hadejia da yanda aka kaiwa Sarkin Hadejia Haru Bubba Labarin Muhammadu. Harda Asalin Jafi da ake Ran sallah A kusa da Masallacin Juma'a. Muhammadu na Allah Ruwan kogi Tafi sannu sannu Wanda yayi wargi Ya Halaka. Giwa ta gama da Masu Karfi Ta wuce.
HADEJIA A YAU The Government and Society of Hadejia in the 19th Century: The government of Hadejia in the 19th century, like other emirates of the old Sokoto Caliphate, was based on autocracy. The emir who was a spiritual as well as temporal head was at the helm of affairs. He was assisted in governing by a class of officials or titleholders who were resident in his court. It was only the Sarkin Auyo who was permitted to stay outside the headquarters: he lived permanently at Auyo town. The composition of these titIe holders or Hakimai was made up of 'ya'yan Sarki (Princes), Dangin Sarki (emir's relatives), Barorin Sarki (clients), and Bayin Sarki (slaves). The structure of this emirate's administration was never dominated by the "Fulani ruling caste", since the heterogeneous nature of the area was taken into cognisance in the distribution of both civil and military offices. For example, during Sambo's reign the title of Madaki was held by a Bamange and that of Galadima was given to a Ba-Auyaki, both non-Fulani tribes. Militarily, the emir was the Commander-in- Chief of the emirate, delegating his function in practice to Sarkin Yaki (Captain General or War Chief), Jarma (Chief of the Brave Ones), Madaki, Sarkin Arewa and other war chiefs. The composition of the entire military force was made up of courtiers, title-holders and their household slaves, Dogarai (the emirate's bodyguards) and contingents from the "fiefs". Hadejia had two broad sectors of the army: the cavalry (Barade) and foot soldiers. Militarily the emirate was considered to be the strongest emirate east of Kano. This reputation it enjoyed and enhanced right from the days of the Buhari Revolt up to the coming of the British.

KUNGIYAR HADEJIA INA MAFITA TA KARBI BAKUNCIN KUNGIYAR JIGAWA NORTON WEST..

Daga Nasiru Kainuwa Hadejia.  Ziyarar wakilai da ga gamayyar ƙungiyoyin masarautar Ringim, zuwa ga ƙungiyar Hadejia Ina Mafita Initiative a ...